settings icon
share icon
Tambaya

Mece ce zuwan Yesu Kristi na biyu?

Amsa


Zuwan Yesu Kristi na biyu shine begen masu imani cewa Allah shine mai iko akan komai, kuma mai aminci ne ga alkawura da annabce-annabce a cikin Kalmarsa. A zuwansa na farko, Yesu Kiristi ya zo duniya kamar jariri a komin dabbobi a Baitalami, kamar yadda aka annabta. Yesu ya cika yawancin annabce-annabcen Almasihu yayin haihuwarsa, rayuwarsa, hidimarsa, mutuwarsa, da tashinsa. Koyaya, akwai wasu annabce-annabce game da Almasihu da Yesu bai cika ba tukuna. Zuwan Kristi na biyu zai zama dawowar Kristi don cika waɗannan annabce-annabcen da suka rage. A zuwansa na farko, Yesu Bawa ne mai wahala. A dawowar sa ta biyu, Yesu zai zama Sarki mai nasara. A zuwansa na farko, Yesu ya zo cikin ƙasƙancin yanayi. A dawowarsa ta biyu, Yesu zai zo tare da sojojin sama a gefensa.

Annabawan Tsohon Alkawari basu bayyana wannan banbanci ba a tsakanin zuwan su biyu. Ana iya ganin wannan a cikin Ishaya 7:14, 9:6-7 da Zakariya 14:4. Sakamakon annabce-annabcen da suke neman su yi magana ne game da mutane biyu, da yawa daga cikin malaman yahudawa sun yi imanin cewa za a sami Almasihu mai wahala da Masihu mai nasara. Abinda suka kasa fahimta shine Masihu guda ɗaya kuma zai cika duka matsayin. Yesu ya cika aikin bawan da yake wahala (Ishaya sura 53) a zuwansa na farko. Yesu zai cika matsayin mai ceton Isra’ila da Sarki a dawowar sa ta biyu. Zakariya 12:10 da Wahayin Yahaya 1: 7, suna kwatanta dawowar ta biyu, duba baya ga an huda Yesu. Isra'ila, da duk duniya za su yi makoki don ba su karɓi Almasihu ba a farkon zuwansa.

Bayan Yesu ya hau zuwa sama mala'iku sun bayyana wa manzannin “Ya ku mutanen Galili, don me kuke tsaye kuna duban sama? Yesun nan da aka ɗauke daga gare ku aka kai shi Sama, zai komo ne ta yadda kuka ga tafiyarsa zuwa Sama.” (Ayukan Manzanni 1:11). Zakariya 14:4 ya bayyana wurin zuwan na biyu kamar Dutsen Zaitun. Matiyu 24:30 ta ce, “A sa'an nan ne alamar Ɗan Mutum za ta bayyana a sararin sama, duk kabilan duniya kuma za su yi kuka, za su ga Ɗan Mutum yana zuwa kan gajimare, da iko da ɗaukaka mai yawa.” Titus 2:13 ta bayyana dawowar ta biyu kamar “bayyanuwar ɗaukaka”.

Zuwan na biyu ana maganarsa dalla dalla a cikin Wahayin Yahaya 19:11-16, “Sai na ga sama ta dāre, sai ga wani farin doki! Mahayinsa kuwa ana ce da shi Amintacce, Mai Gaskiya, yana hukunci da adalci, yana kuma yaƙi. Idanunsa kamar harshen wuta suke, kansa da kambi da yawa, yana kuma da wani suna a rubuce, wanda ba wanda ya sani sai shi. Yana saye da riga wadda aka tsoma a jini, sunan da ake kiransa da shi kuma, shi ne Kalman Allah. Rundunonin Sama, saye da lallausan lilin fari mai tsabta, suna a biye da shi a kan fararen dawakai. Daga cikin bakinsa wani kakkaifan takobi yake fitowa, wanda zai sare al'ummai da shi, zai kuwa mallake su da tsanani ƙwarai, zai tattake mamatsar inabi, ta tsananin fushin Allah Maɗaukaki. Da wani suna a rubuce a jikin rigarsa, har daidai cinyarsa, wato: SARKIN SARAKUNA, UBANGIJIN IYAYENGIJI.”

English



Koma zuwa shafin gida na Hausa

Mece ce zuwan Yesu Kristi na biyu?
© Copyright Got Questions Ministries